Sunday 16 April 2017

CIN AMANA KO FANSA

📓📓📓📓📓📓📓📓📓
            *CIN AMANA*
                    *KO*
                *FANSA*
📓📓📓📓📓📓📓📓📓



Zahra Muhammad Mahmud


*pure moment of life writers*
         *pml*


*page 4-5*



Koda suka isa gida Khairat gaban mirror taje ta tsaya tana k'arewa kanta kallo,can kuma tasake fashewa da kuka ta fad'a kan gadonsu,Fatima wacce dariya tagama kamata da k'yar ta daure tace.

"Sis lafiyarki k'alau kuwa?, wai kukan me kikeyine haka?".

Cikin kuka Khairat tafara magana.

"Haba ki dubenifa wai ace duk had'uwar nan tawa manyan mutanennan bawanda yakalleni bare yace yana sona,nibama wannan ne yake sani kukaba more than 3hours nad'auka ina Kwalliyar nan Amman wai ace me hotone kawai na burge ay dole nay kuka,"taci gaba da kukanta harda majina.

Fatima ko inbanda dariya ba abinda takeyi sabida gaba d'aya takasa magana abun yabata dariya sosai. Fita Khairat tayi a d'akin sabida dariyar da Fatima take mata.

Tunda wannan D'an majalisa ya amshi number Fatima se yau ya gwada kiranta kimanin sati guda kenan da had'uwarsu,lokacin daya kira suna zaune ita da Y'ar darunta wato Khairat suna labarin wani littafi da ake rubutawa na online writers nawata marubuciya Zahra Muhammad mahmud me suna *Allah gatan bawa*.ajiyar zuciya Khairat tayi tace.

"Ya Ubangiji nima kasa nayi irin wannan dacen da jarumar littafinnan ilham tayi,nima nasamu miji kamar Anwar Tunda nima kyakkyawace",ta fad'i harda d'aga hannu sama,dariya Fatima tayi tace.

"Allah yataro minke Sister".

k'arar wayar Fatima ce takatse musu hirar,number tagani da kamar karta d'aga cande kuma ta d'auka,tace,

 "Salamu alaikum".

"Wa'alaiki salam ya ma'abociyar natsuwa da hankali,".

Tsigar jikinta seda ta tashi sabida jin daddad'ar muryar me maganar, katseta yayi da cewa.

"Am sorry princess tunda na amshi numberki ban kiraki ba se yau please ayimin afuwa, al-amurane suka sha kaina tuba nake sarauniyar mata".

Murmushi ne ya sub'ucewa Fatima kamar yana kallonta,sabida ba k'arya muryarshi kad'ai dataji tasa taji takamu da son mamallakin wannan murya.cikin salo najan hankali tace.

"Ammaka afuwa duk da bansan dawa nake maganaba pls can you tell me more about your self?".

muryarta se yau yake k'ara jin dad'in muryar da k'yar yace.

"Am Hydar Jibrin Lamid'o, wanda yaturo kibashi number ranar bikin friend d'inki Jameela sati guda daya wuce, so inbazaki damuba inason address d'inki dannazo mugaisa kinji pls badan na isa ba sedan Allah."

Fatima tunani tashiga yi agame da sunannashi dan ita tabbas tasan d'an majalisarsu me wakiltarsu a Abuja sunanshi kenan,toko suna ne yazo d'aya?, ko shine dakanshi?,kai mezeyi dani?bashi bane.haka tadunga tunani ita kad'ai shine dayaji shurun tayi yawa yakatseta.

"haba princess wlh ba cutar dake zanyiba kidaure kibani address d'in kinji zuwa anjima da yamma zan shigo mugaisa,"ba musu Fatima tai mishi address d'in gidansu,yay mata godiya yace se yazo anjiman sukayi sallama. Tana ajiye wayar Khairat wacce tun d'azu kallonta kawai takeyi tace.

"Sister wlh tunda nake bantaba ganin budurwa me arha irinkiba, haba don Allah shikenan kowa yataya ba jan aji kike siyarwa Wlh kina badamu,nide gani nake yadda akasan address din gidanmu ta dalilinki ko gidan gomna se haka ace ayi mutum sam bajan aji wlh kigyara halinki ni nafara gajiya da hakan,"tafad'i har da tsakinta.

murmushi Fatima tayi tace.

"Sister kenan shi wannan Jan ajin dakike magana ba irinshi addininmu yakoyar damuba, sabida duk wacce takeyin irinshi ba sunanshi Jan ajiba wulak'anta halittar Allah sunanshi wanda kinsani nasani ba abune me kyau ba dan haka ni inde hakan danakeyi shine rashin aji to nayarda har atashi duniya bazanyi ajiba arayuwata".

"to Allah ko yakyauta miki wlh,yanzu kuma wanne d'an wahalar ne yakiraki?"inji Khairat.

"Wanda ya turo nabashi number na ranar dinner d'in Jameela Habib,yacema zezo anjima mu gaisa."


Dariya Khairat ta kwashe da ita tace.

"lalle Sis wato ke baki d'au ishara akainaba kina ganin duk kyannan nawa me hoto kawai na burge agurin,ayko tunda haka ko tafaru akaina Allah Sis may be megadin gurinne ya turo kibashi number,"tasake fashewa da dariya.

Fatima itama dariyar takeyi tace,"to in megadine seme?, shiba mutum bane?,koko shi ba Allah ne yayi shiba?,kinga rabani da wannan shirmen naki koma waye ni ina maraba dashi,tunda wannan Karon gurina megadin zezo ay da sauk'i bagunki naturoshi ba bare ki tsine mishi son ranki."

Wata shewa Khairat tayi tace, "ina wlh Sis ayni nafi k'arfin irinsu sede ke, ni ay matar manyace ko kin mantane?".

"Natuna matar Donald Trump,"
Fatima tabata amsa tana dariyar tsokana ita ta d'auka Khairat zataji haushi ga mamakinta seji tayi Khairat tarungumeta tana fad'in.

"Wlh Sis kinyimin fata me kyau,ni abin yace yana sona wlh auransa zanyi baruwana da kafircinshi yayi addininshi nayi nawa,nazama First Lady a America wai ranar ina zansa kaina dan dad'i".

Tureta Fatima tayi cike da mamaki tace.

"Sis ke har son kud'in naki yakai ki auri kafiri matuk'ar yanada kud'i kuma sunanki ze fita as celebrity a duniya wato zaki iya auransa kenan?Allah yashiryaki lamarinki yafara bani tsoro wlh,"tafad'i cike da damuwa.

Khairat ko ko a jikinta mik'ewa tayi tad'auki gyalenta tace ni natafi gidan su Zainab Umar zan amso note book d'inta na chemistry na kwafa sabida banida complete note sena dawo Ummu shuhada",tafad'i tana dariya tafice a d'akin tabar Fatima baki bud'e.


5:30pm Hydar yazo gidansu Fatima,acikin wata arniyar motarshi Range Rover new model fara tasha tinted glass bak'i sosai bame ganin naciki,numbar motar sunane ansa  Hydar 1,gashi yayi shiga ta alfarma wacce duk macen data ganshi seta koka ba laifi Hydar kyakkyawane ajin farko dan yafi Fatima kyau nesa ba kusaba.

Kiranta yayi a waya ya shaida mata gashi ya iso.


Hijabi tasa bayan tad'an k'ara gyara fuskarta tafesa turare tafito zuwa k'ofar gidan, lokacin Khairat bata dawo daga anso littafinba.

Fatima koda tafita wata arniyar mota tagani a k'ofar gidansu wanda batai tsammanin acikinta me nemanta yazo ba, waige waige takeyi tarasa ina wanda yazo gurinnata yatsaya,shiko daga cikin motar K'are mata kallo yakeyi yana k'ara godiya ga Allah daya had'ashi da nutsatsiyar yarinya irinta,ganin tana nemanshine yasa yakirata a waya yace gashinan acikin motar dake gabanta,dasauri yaga ta kallo motar sannan tace.

"to kafito mana,"yace.

"Princess inda hali mushiga daga cikin gidanku in akwai inda zamu zauna peacefully banason intsaya awaje kowa yazo yaganni kinji pls,"amsa tabashi dacewa.

 "sekace mara gaskiya".

dariya yayi wacce tasa Fatima k'ara fad'awa kogin sonshi yace.

"watak'ila hakanne banida gaskiyar ay ba laifi bane dan na nemi mafaka daga gareki," murmushi tayi sannan tajuya cikin gidan,gurin maman Khairat tanufa tace mata tayi bakone tade fad'amata yadda sukayi dashi yanzu tanason abata key d'in sit room d'in Abban su,jamata kunne maman tayi sosai akan tade tsare mutuncinta sannan ta bata key d'in.

zuwa tayi tabud'e sannan tafita takirashi awaya tace yafito to yak'araso sushiga daga ciki, ga mamakinta me makon taga yafito setaga ya tuk'o motar har zuwa k'ofar gidan sosai sannan yay parking yafito.

Hasbunallahu wani'imal wakil itace kalmar dake fita a bakin Fatima sanda tai arba dashi,ba iya kyan shine ya ruda ta ba a'a sanin wayeshi a jihar kaduna shine ya rud'ata, shiko se murmushi yake sakar mata me kashe zuciya har yak'araso gurinta bata saniba,Ta tafi tunani hura mata fuska yayi sannan tadawo daga duniyar data tafi,kashe mata ido d'aya yayi yad'aga gira yace.

"yadai princess wannan kallo ay sekisa nafad'i ayimin dariya", kunyace takamata da k'yar tace mishi su shiga daga ciki.
       
koda suka shiga gaisheshi tayi sannan takawomishi drinks kad'an yasha sannan yace.

"Princess the way you act for the first time dakika ganni nasan kinsan koni waye so no need natsaya ina cemiki nine wane, kawai abu d'aya zan iya sanar dake shine tunda naganki Allah ya jarabceni da sonki so me tsanani,don haka nake rok'on alfarmarki kisoni koda rabin son danake miki ne pls,"yafad'i cikin sigar tausayi.

Fatima bata hana kanta abinda takeso inde be sab'ama addini da al-adar ta ba don haka bata jamishi raiba ta amshi soyayyarsa kuma dama Hydar ba irin mazan da ake cewa kaje senayi shawara bane.

yaji dad'in amsar soyayyarshi datayi batare data wulak'antashiba, abinda y'anmata suka d'auka wai Jan ajine,hirarsu ta soyayya suka shigayi duk da Fatima kunya ta isheta takasa sakin jikinta dashi shine ke mata hirar.


Khairat ta dawo daga amsar littafin lokacin datayi arba da motar Hydar a k'ofar gidansu seda tayi tuntub'e ta fad'i sabida kallon datakewa motar,Allah yasota bakowa agurin da sauri ta Mik'e tashiga cikin gidan tana waigen motar.
   tana tunanin gurinwa me motar yazo a gidansu,zata wuce cikin gidane taga takalmin Fatima a k'ofar sit room d'in Abban su da kamar ta wuce se tafasa taje tayi sallama a k'ofar d'akin,Fatima ce ta amsa gami da cewa.

 "yauwa ga Sis d'ina ta dawo danake baka labarinta Sis kishigo mana kintsaya",bud'e k'ofar tayi tashiga da sallamarta.

Ya Ilahi!!!!.

ita Khairat ta furta sanda tai arba da fitaccen d'an siyasa kuma d'an majalisa me wakiltar kaduna South a Abuja mutumin da Nigeria ansanshi sabida motion d'in daya kaiwa majalisa, uwa uba shine mutumin data dad'e tana mafarkin samunshi a matsayin mijinta na aure.

Zama takeso tayi akan kujera amman dayake arud'e take zamewa tayi tafad'i ak'asa sabida hankalinta nakanshi, dasauri Fatima tazo takamata Ta tashi itako ko ajikinta k'ok'arin gaisheshi takeyi,amsawa yayi bayabo ba fallasa danshi mutum ne miskili ba kowa ke ganin fara'arshiba.

memakon dasuka gaisa tabasu guri ay ina k'ara shishshigewa take tana kwarkwasa ita game kyau hakan beyiwa Hydar dad'i ba don haka sallama yay musu gami da cewa Fatima.

"My Princess zamuyi waya innaje gida kinji take care of your self OK".

amsa mishi tayi da Allah yakaishi gidan lfy Ta gode da ziyara.

bunch d'in one thousands yaba Khairat yace, "to k'anwarmu ga wannan kisha ice-cream,"juyawa yayi yafita bayan yabata kud'in,har gurin mota ya tilastawa Fatima tarakashi sannan sukayi sallama ya wuce.


Maman Yusuf

No comments:

Post a Comment