Monday 17 April 2017

CIN AMANA KO FANSA

πŸ““πŸ““πŸ““πŸ““πŸ““πŸ““πŸ““πŸ““πŸ““
          *CIN AMANA*
                   *KO*
               *FANSA*
πŸ““πŸ““πŸ““πŸ““πŸ““πŸ““πŸ““πŸ““πŸ““



Zahra Muhammad mahmud


*pure moment of life writers*
          *p.m.l*


*Dedicated to My sweet Aunty,Hajiya Jameela (meelmoh)C.E.O meelmoh magazine Allah yak'ara d'aukakaki farar mace alkyabbar mata,Aljanna me masoya dayawa nagode.*


*page 6-7*


Fatima nadawowa daga rakiyar Hydar,Khairat tajata zuwa d'akinsu,ko zama bata bari sunyiba tace,

"Sis wai nufinki ke Hydar yakeso?,kuma shine wanda ya amshi numbern ki?,pls ineed more explanation."


"Why are you asking me all those questions?,ina tunanin bakya buk'atar k'arin bayani sabida tambayoyinki tafe suke da amsoshinsu,tunda idonki yagane miki,I hope you understand what I mean?".

Ajiyar zuciya tayi ta nemi guri ta zauna tayi tagumi,Fatima ce ta dafata tace,

"Sis are you ok?".

Asanyaye tace,"yes am ok, but Sis let me ask you  something".

Fatima tace ,"uhum inajinki".

"Dama ba wani abu bane tambayarki zanyi kuma kema kina sonshi?,sannan zaki iya auranshi?"Khairat tafad'i kamar me shirin yin kuka.

shewa Fatima tayi tafad'a jikin Khairat d'in tace,

"Wlh Sis har kinbani wata bazawarar dariya,to ke ko idona kika kallah ay kinsan na mato akanshi,wacce macece aduniyarnan zata samu kamar Hydar tace bata so ay wlh sede in bata samuba,ni wlh yanzu banida wani buri daya wuce naga na aureshi badan kudinshiba sedan nagartattun halayansa wanda najima ina burin miji me irinsu, ay Sis ki tayani addu'a kawai Allah yabarni tare dashi kusha biki,"tak'ara rungume Khairat cikin farin ciki mara misaltuwa.

Khairat jitayi kamar ta watsamata wuta ajikinta,a sanyaye tace,"Allah yanuna mana lokacin natayaki murna y'ar uwa".

Ranar Khairat batayi bacciba sabida tunanin yazatayi, tanason y'ar uwarta matuk'a amman batajin son datakema Fatiman yakai wanda takema zuciyarta,tanaji zeyi wuya tabar Fatima ta haramta mata abinda ta dad'e tana nema wato Hydar.

Koda safiya tayi zasu tafi makaranta,khairat sam babu walwala atattare da ita gaba d'aya ta sauya,cike da kulawa Fatima tace.

"Sister alamu sun gwada baki da lafiya don Allah ki sanar dani meke damunki,kinsan banison damuwarki hankalina tashi yake don Allah ki sanar dani ko hankalina ze kwanta".

Azuciyarta tace,"kece damuwata Fatima,kuma kece ciwon dake damuna,neman hanyar dazan magance hakanne yasa kika ganni haka",amman afili setace mata,"Wlh da ciwon kai na kwana Sis shiyasa kika ganni haka amman ba abinda yake damuna".


Haka suka tafi makarantar Fatima se tausayawa Khairat takeyi,bata zargi komaiba game da sauyawar Khairat d'in daga jiya zuwa yau.

Son da Fatima takewa Khairat rai ne kawai bazata iya bata ba jinta take har ranta burinta ta faranta mata akullum dan farin cikin Khairat shike sata farin ciki.

Ana tasosu daga makaranta gida suka dawo ga mamakin  Fatima Hydar tasamu a k'ofar gidan yana jiranta,tun kamin Ta k'araso ya iso inda take jakar makarantarta ya amsa yace.

"Barka da dawowa me d'akina ya karatu,?ina fatan baki wahala ba?".

kunyace duk ta rufeta ganin irin kallon dayake mata murmushi kawai takeyi ta rufe fuskarta a hijab,takasa bashi amsa.

Khairat jitayi kamar ta kurma ihu dan bak'in ciki ga wani azababben kishi daya tasomata,maganama takasa. Hydar ne ya waigo ya kalleta yace, "k'anwarmu ungu jakar Auntyn ki kishigar mata da ita yanzu Zata shigo itama".yamik'a mata jakar,yata iya dole ta amsa tashige gidan,shikuma da Fatima suka shiga daga cikin gidan amman ba sit room ba.

Agurguje suka gaisa yace ze wuce Abuja ne yanzu shine yace bari yazo yaganta dan inyatafi zekai two months acan sabida zeyi wata tafiyane daga cand'in,Fatima ranta besoba hakade yay ta kwantar mata da hankali da alk'awarurruka masu yawa har tak'aitaccen tarihin rayuwarsa seda yabata,itama akunyace tabashi nata.

"Princess zamu fahimci juna kamin nadawo sabida ina dawowa zan turo zancan auranmu bawani lokaci nakeso ad'aukaba nak'osa naganki gidana wlh kuma zuwa lokacin kungama Waec d'inku dan haka don Allah ki amince muyi aure Kya ci gaba da karatun agidana".

murmushi tayi tace, "bakomai Allah ya zab'a mana abinda yafi zama alkha'iri Allah kuma yakaika Lfy yadawomin dakai lafiya",tana gama fad'a tak'ara rufe idonta tana dariya mara sauti,shima dariyar yayi yace, "Ameen my Princess".

Kayan dayayomata shopping su yadunga fito dasu almajirai suka shigar mata dasu cikin gida haka sukai sallama kowa na bak'in cikin rabuwa da d'an uwansa.

Khairat ganin kayan da Hydar yakawowa Fatima shi yasa tak'ara kwad'aituwa da son mallakarsa,numfashinta har rik'ewa yakeyi inta tuno da irin kallon dasukewa juna d'azu tsakanin Fatima da Hydar.


*Waye Hydar*

Hydar Jeebrin Lameed'o shine cikakken sunansa,d'ane guda ga Alhaji Jeebrin Lamid'o.

Shikad'ai Iyayensa suka haifa shiyasa yataso cikin so da kulawa,hydar miskili ne na ajin farko baruwanshi dashiga sabgar dabata shafeshi ba shi mutumne meson girma,kuma yanada tsaron Allah duk abinda addininsa yahana yana k'ok'arin kiyayewa yana takatsantsan da imaninsa kud'i da mulki basu sa ya kauce hanya ba.

Mahaifinsa babban ma'aikacin gomnati ne ajihar kaduna amman asalinsa d'an jahar Adamawa ne acikin garin michika zamane yakawosa kaduna kuma anan ya had'u da Hajiya Hadiza wato mahaifiyar Hydar kenan.

Suna zaune acikin wata anguwa me sunshine kinkinau dake garin kaduna.

Hydar cikakken d'an siyasane wanda kowa kesonshi,yayi degree har zuwa Masters duka akan fannin siyasa shiyasa yake yinta bisa tsari, yarik'e muk'amai kala-kala a ma'aikatun gwamnati har zuwa yanzu dayake wakilcin Kaduna South a Abuja.

Hydar  yayi aure da matarshi me suna Maryam Sun haifi yaro d'aya mesuna Haisam inda tasake samun wani cikin gurin haihuwa tarasu bayan ta haifi y'amace inda yariyar taci sunan mahaifiyarta wato Maryam suna kiranta da Iman.

Tunda Maryam ta rasu Hydar yarasa natsuwarsa sabida Maryam tana da kirki ga hak'uri duk abinda yakeso shi take mishi shiyasa yakasa mantawa da ita,seda iyayensa sukai ta nemar mishi taimako daga malamai sannan zuciyarshi ta natsu,amman duk sanda yakalli yaransa se yayi kuka na rashin mahaifiyarsu, yaran na hannun mamanshi ita take kulawa dasu.

Sam Hydar yacire batun aure aranshi kwatsam se yahad'u da Fatima kuma  Allah yajarabceshi da sonta wanda har yasanar da iyayensa yasamu mata in yadawo daga tafiyar nan dazeyi ze turasu aje anemar masa auranta.

cigaban labari

kubiyoni


Maman Yusuf.

4 comments:

  1. Assalam malama zahra, naji dadin wannan labarin, nabude wani website domin kawo novels kala kala wa mutane, Kuma agaskia zanso muyi aiki tare domin ki dinga min rubutu akai ina biyanki pls kimin magana ta WhatsApp 080648618325

    ReplyDelete
  2. Ku sayawa blog Ι—inku domain, sai ku sayi theme a Ι—ora maku, sai ku nemi ads za su riΖ™a biyanku, ni marubuci ne Ι—anuwanku, Sunana Bello Hamisj Ida

    ReplyDelete