Sunday 16 April 2017

SURBAJO

🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
         *SURBAJO*
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀

Zahra Muhammad mahmud

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS(P.M.L.W)*

*page 71-72*

Koda ya'isa gidansu still ranshi abace yake dak'yar ya iya yimusu sallama,

Hankalinsu tashi yayi dasuka gansa ayanayin dabasu saba ganinsaba, tambayarsa suke meyafaru dashi,seda yad'an natsu sannan yafad'amusu abinda yafaru, Dukansu bawanda be firgita dajin labarinba, Daga 'karshe fatan Allah yasa hakan shi yafi alkha'iri suka masa, inda Mahaifinsa ya'kara dacewa, "Ka rage saurin yanke hukunci cikin fushi",amsawa yayi da insha Allahu yadena.

Aisha dak'yar tamik'e tafara neman mayafinta kuka take kamar ranta zefita,ga hannunta dayake mata azabar ciwo ahaka tadaure ta hada iya abinda zata iya d'auka tabarmasa gidansa cike da d'umbin danasani, tabiyewa k'awaye gashi sunkaita sun barota,rasa ina Zata sa kanta tayi,
  Driving take amma ko gabanta bata gani Allah ne kawai yakaita gidansu Lfy, Tanayin parking da gudu tashige cikin gidan tana kuka me tsuma zuciya kan mamanta tafad'a, wacce ke zaune Tana yankan alaiyahu dasauri taajiye wuk'ar Tana tambayarta meke faruwa?,
  Cikin kuka Aisha ke fad'in,"wayyo Allahna Inna nacuci kaina nabiyewa sharrin k'awaye gashi yau sunkaini sunbaro,yau mijina yasakeni had'e da sakamakon bazan sake haihuwaba arayuwata",wani kukan tasake rushewa dashi, Mamanta jikintane yakama rawa kamar mazari jin zancan Al-ameen yasaki Aisha dak'yar ta'iya tambayar Aishan metayimasa?, nanfa Aisha takwashe komai tasanar da Inna, wani gigitaccen Mari Inna tawankawa Aisha har so biyu tuni Aisha tasoma ganin taurari sabida Marine bana wasaba, cikin 'bacin rai Inna tace,
"Aisha gaskiyar Aminune dayacemiki kanki kika cuta to wlh kannakin ko kika yiwa, Aisha yaushe rashin imaninki yakai haka ki iya kashewa mace y'a tun aciki keko mekike nema wandau Aminu yagaza gurin yimiki, wlh kinyi rashin mijin da keda samun kamarsa har abada azamaninnan, natayaki murna seki zo mujeru agidan arasa gane wacece uwar acikinmu, zancan bazaki haihuba kuma sakayyace Allah yama wacce kika zalinta".

Maganganun Inna sunshigi Aisha sosai take numfashinta yafara barazanar d'aukewa, kamin Inna tayi wani yunk'uri tuni Aisha tazube ak'asa sumammiya,
  Agigice Inna tayi kanta tana kiran sunanta Amman ina ko numfashi batayi, ruwa tad'ebo ta yayyafamata shima abanza, arud'e Inna tayi k'ofar gida neman taimakon jama'a,nan da nan  aka shigo akad'auki Aisha zuwa Asibiti.

Al-ameen kwanansa d'aya yajuya Abuja,
  Cike da farinciki Surbajo ta tarbeshi domin tayi murna da dawowar tashi,abinci masu rai da Lafiya ta gabatar masa bayan yayi wanka yashirya sannan suka dawo dinning yaci abincin,

Falo suka dawo suka zauna Surbajo na mak'ale dashi, yayinda Yusuf yana makaranta dan ansashi a makarantar,
Tambayarshi take,"dear meyasa kadawo da wuri"? murmushi kawai yamata dan bayason yafad'amata abinda ze d'agamata hankali,
  Daminshi tayi da tambayar, "dear nagama kasauya kamar baka cikin walwala meke faruwane? don Allah kasanar dani",

Ganin tashiga damuwane yasa,yakwashe duk abinda yafaru tasanar da ita,afirgice tamik'e daga jikinshi tana maimaita kalmar," Itace tayi sanadin mutuwar Babyna ?me muka yi mata da zafi har haka dazata za'bi rabani da abinda nafiso arayuwata? menayimata!!!?
  Durkushewa tayi Tana kuka Al-ameen behanataba yabarta tayi sabida zatafi samun sauk'i a zuciyarta,

Seda yaga tayi dayawa sannan yakamota yana rarrashinta ahankali hartadena kukan,seda take natsu sosai sannan tace,

"Dear sakin dakayiwa Aisha bedaceba sabida cuta de tariga data gama cutar damu babu wani abu dazamuyi mata murama, nide anawa ganin kayi hkr kadawo da ita dakinta zefi dan wlh sakinta bashine mafitaba kuma ni nayafe mata sauran tsakaninta da ran data kashene ranar gobe kiyama kuma kaima inaso kayafemata Don...... Marin daya wanketa dashine yasa takasa karasa abinda zata fada, hankad'eta yayi tafad'i ak'asa bebi takaiba yanunata da yatsa sannan yace cikin kakkausar murya,

 "how dare you Surbajo?she killed my princess and also she destroyed my happiness, and she make you suffer alot,then for all this, now you are looking into my eyes without fair asking me to forgive her  how dare you? That means my  happiness it's doesn't matter to you thanks you so much",
   yana gama fadin haka yajuya yafice daga gidanma gaba d'aya,Surbajo kuka ta rushe dashi anan gurin daya yardar da ita, Sam ita bataga aybin maganartaba dahar zeyi fushi da ita har haka, kukanta taci gaba dayi.

Maman Yusuf
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
         *SURBAJO*
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀

Zahra Muhammad mahmud

*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS(PML)*

*page 73-74*

Surbajo gajiya tayi da zama afalon tamik'e ta shige d'akinta.

Al-ameen ko tunda yafita yabar gidan ranshi a'bace yake,milonian park yaje domin yasha iska,gurin da ba hayaniya sosai yasamu yazauna yana tuno abinda Aisha da Surbajo suka masa ransa nak'ara 'baci,idonsa a lumshe yake yana jin dad'in iskar dake kad'ashi,sallamar da'aka masace tasa ya bud'e idanuwannasa.

Wata budurwace wacce shekarunta bazasu gaza ashirin da biyarba,sanye take cikin wata purple din doguwar riga irin me kama jikinnan,ta yafa wani d'an siririn mayafi akanta fari,fuskarta sanye cikin wani bak'in glass yayin da abakinta kuma tana taunar cwingum, ba laifi tana da kyau da diri dede misali, ita yagani tsaye akansa fuskarta d'auke da murmushi,cigaba tayi da cewa,

"In bazaka damuba please zan iya zama anan,"tanuna kusa dashi,shiko Al-ameen binta kawai yake da ido tun kamin yace ta zaunan harta zauna kusa dashi,dubanta yayi sannan yace,

"Baiwar Allah lafiya?zakizo ki zauna anan ko aykoki akayi?," wani shu'umin murmushi tayi gamida fari da idonta tace,

"Wlh kaso kad'an bani dariya wato ni ban isa inzo gunka zuwan kainaba sede idan aykoni akayi,to zancan gaskiya bawanda ya turoni gurinka,ganinka nayi da alamun damuwa a tattare dakai shiyasa nace bari inzo ind'ebemaka kewa watak'ila inyi nasarar rabaka da damuwar dake ranka."

Al-ameen kallonta yayi sannan Yace, "ni nace miki inada damuwa?,kuma inaga ay in ina buk'atar ad'ebemin kewa nafiki sanin inda yadace inje ad'ebemin d'in,dan haka inbazaki damuba kibar gurinnan nazo nasha iskane kinzo kintaremin so please kid'an barni na huta".

Wani irin juyi tayi wanda yatilasta jikinsu had'uwa,tak'ara matsawa sosai jikinshi,faruwar hakan ne yasa jikin Al-ameen mutuwa yakasa wani kyakkyawan motsi,magana tafara tana shafo gefen fuskarshi cikin salo na yaudara tana wani tutturo kirji gaba wanda harsuna gogar jikin Al-ameen d'in tace,

"Haba namijin duniya gaka de kamar kawaye amman kanaso kabada maza, ay soyayyace take sawa daga kallon mutum kagano abinda yake damunsa,nasan kana buk'atar kulawar mace awannan lokacin so please let me try my best wajen taimaka maka,"

Dakyar Al-ameen yace,"you are welcome once again thanks for the care and concern,"murmushin cin nasara tayi sannan tace,

"Sunana jameela amma friends d'ina suna kirana da aji dad'i,ina zaune anan garin Abuja badan komai ba sedan naji dad'i, so ihope zakayi joining d'ina domin kaima najiyar dakai dad'in dake tattare dani."duk maganarnan datayi tanayine tana shashshafo Al-ameen gami da yimasa abubuwan da dole duk namiji me lafiya se hankalinsa yatashi.shiko sha'id'anne yak'ara samasa jin dad'in abinda take masa shiyasa sam  beyi yunk'urin hanataba.cikin salo irin na rikakkun karuwai Ajidad'i tadunga yaudarar Al-ameen harseda yabata number wayarsa sannan yadauketa yamata shopping sosai sannan yakaita gidansu ita da wata k'awarta mesuna  Ayna'u cleaner.

Da isarsu k'ofar gidan yayi parking dan yace sauri yakeyi baze shiga cikiba se next time,nanfa Ajidad'i tadunga yaudararsa harseda ya shiga,koda ya shiga gidan  bata saukeshi afolo ba seda ta dangana da d'aki sabida ita tunda taganshi taji tana sha'awarshi burinta kawai takawar da wannan sha'awa data kamata tashi,suna shiga kulle kofar tayi sannan tafara cire kayan jikinta,Al-ameen binta yake da kallo shed'an nak'ara k'awatamishi surarta,dasauri yaje yarungumeta suka fara romancing d'in juna har zuwa suka fad'a kan gado,Ajidad'i gabad'aya tagama k'osawa komai ya kankama dan itan irin matannanne masu jaraba,sede kash tuni tsaron Allah ya fad'owa Al-ameen azuciya jikinshi rawa yadunga yi yanata a'uziya neman tsari daga shed'an, tureta yayi ajikinshi yamik'e tsaye zuwa lokacin har hawayen  takaicin abinda yayi sunfara biyo fuskarshi ga Surbajo data fad'o masa a rai tabbas yau dayayi zina da ajidad'i  da besan da wanne ido ze kalleta ba, dan yasan dede gwargwado Surbajo nabiya masa buk'ata duk da k'ank'antar shekarunta tana jure duk buk'atunshi batare data gajiba ko taimasa k'orafi,kotakan Ajidad'i beyiba  yajuya yafice daga d'akin ranshi nak'una yaja motarshi yanufi gida gurin Surbajo.

Abangaren Ajidad'i kuwa tafiyar Al-ameen bak'aramin d'aga mata hankali tayiba dan gaba d'aya sha'awarta tagama tasowa gashi yagudu yabarta rasa ina zatasa kanta tayi,kuka tasa iya k'arfinta wanda yajawo hankalin Cleaner zuwa gurinta,da sauri Cleaner tashigo d'akin ganin Ajidad'i tsirara bedametaba illa k'arasawa gurinta datayi tana tambayarta meke faruwa, ganin takasa bata amsa ne yasa Cleaner ta fahimci abinda ke damun Ajidad'i danhaka bata 'bata lokaciba tacire kayan jikinta tajawota jikinta suka shiga aykata masha'a,wa'iyazu billah.

Seda komai yalafamusune Ajidad'i taba Cleaner labarin abinda yafaru tsakaninta da Al-ameen,tsaki Cleaner tayi sannan tace,

"wannan ay abune mesauk'i bade yabaki number d'insa ba ay anwuce gurin kedai kawai ki kwantar da hankalinki."

Maman Yusuf
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
       *SURBAJO*
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀


Zahra Muhammad Mahmud


*PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*
        *P.M.L*

Afuwan nayi mistake din number ne


*page 75-56*

Yana isa gida a kitchen yasameta tana girki, rungumeta yaje yayi ta baya dasauri Surbajo tajuyo dan ganin waye yarungumeta, ganin Al-ameen ne yasa tasaki ajiyar zuciya.

Juyowa tayi Itama tarungumeshi tana fad'in,
"i know my dear bazaka iya fushi daniba don Allah kayafemin Inna b'atamakane bazan sakeba",
D'ora hannunshi yayi akan bakinta alamar tayi shuru sannan yak'ara sassauta muryarshi yace,

"Baki b'atamin ba baby kawai nayi fushine sabida ina ganin kamar baki damu dani bane Shiyasa amman yanzu komai yawuce kiyi hk'r kinji my lollipop,"yafad'i yana kaimata kiss abaki,janyewa tayi ajikinshi sannan tace,

"To yazancan dawo da Aisha d'akinta da nayi maka d'azu,?kaamince ko har yanzu baka yardaba,?"
Kunnenta yaja da hannunsa yana murmushi  yace,

"Ya na iya da gimbiyata tunda kince ta dawo naamince amman ba yanzuba gaskiya".

"Se yaushe",Surbajo ta tambaya.

"Se nasa ajiya anan"yashafo cikinta yana dariya,ture hannunshi tayi zatayi magana yadakatar da ita dacewa,

"Wlh this is my final decision Inkuma baki aminceba to nafasa dawo da itan",dasauri Surbajo tabashi amsa da cewa,

"Aradu na amince Kado,"dariya gaba daya suka sa sabida tuno da irin maganarta tada da takeyi.

Rayuwa suka cigaba dayi cike da so da k'aunar juna, kullum Surbajo na k'ara rok'onshi yadawo da Aisha shiko dagewa yayi akan se Surbajo tayi ciki sannan ze dawo da Aisha,hakanne yasa Surbajo tafara tsayuwar dare tana rok'on Allah yabata ciki dan Aisha tadawo d'akinta.

Bangaren Aisha kuwa ciwon zuciyar tane yatashi kuma tashi me tsanani, dan Inna har ta cire ranta akan Aisha dan kowa yaganta ze d'auka inyafita kamin yadawo ze tarar ta mutu,batasan waye akantaba ko numfashi ta oxygen take shak'arsa abun gwanin ban tausayi,Inna da sauran k'annanta sede susata agaba suna kuka,likitocin dake dubata sunayin iya bakin k'ok'arinsu dansuma suna tausaya mata.


Ajidad'i yau tashirya kiran Al-ameen dan haka bata batayi tunanin komai ba takirashi,seda takira yafi so biyar ba'a d'aukaba can taji yad'aga ,tace,

"Haba namijin duniya ba fad'a me yakawo gaba kuma,"tunda ta fara magana yaganeta ranshi ne yay masifar baci da kiran data mishi sabida ta tuno mishi abinda yafaru tsakaninsu katseta yayi da cewa,

"Banyi mamakin kiran da kikamin ba sabida nasan wacece ke,kuma dama duk inda karya take ba'a rabata da bin maza, nayi danasanin had'uwa dake Jameela,ke shaid'aniyace me kai jama'a wuta, daga yau se yau inkika k'ara kirana sena miki abinda baki zataba stupid kawai, be jira amsartaba yakashe wayar yana huci kamar tana gabanshi.

Itako Ajidad'i bata d'auki zancan nashi serious ba kullum seta kirashi baya dauka kuma bata denaba,dataje gurin bokanta yamishi asiri hkr yabata yace baze iya ba sabida Al-ameen akwai tsari ajikinshi.
   Duk da haka bata hkr ba sabida tasha alwashin Seta lashi zumarsa,ci gaba tayi da kiranshi shi kuma yak'i yasata a blacklist ne acewarsa ita bata isa tasashi yin hakanba tai ta kiranshi harta mutu.


Allah maji rok'on bawa.

Yau Surbajo da zazzab'i ta tashi ga kasala,danko Yusuf takasa yimasa wanka Abbanshine yashiryashi driver yatafi kaishi makaranta,sannan yadawo kanta,
 Wanka yamata Itama yashiryata sannan yabata abinci taci tana gama ci ama'i yataso mata da gudu tayi cikin bayi tafara kwara aman,binta yayi bayin yataimaka mata ta gyara jikinta sannan ya wanke inda ta b'ata suka fito, be jira komai ba yad'auketa suka nufi Asibiti,awon farko likita yatabbatar musu da tana da ciki har na wata biyu, ga mamakin Al-ameen Surbajo tafishi murnar samun Cikin har sujudul shukur tayi, murna sukayi bata wasa ba babu kamarma Surbajo sabida burinta ze cika nason Al-ameen yadawo da Aisha.

Suna isa gida tasamishi daru akan wlh seyaje Kaduna aranar yadawo da Aisha in ba hakaba wlh seta cire cikin,hankalin Al-ameen inyayi dubu yatashi rasa yazeyi da ita yayi dan yasan ta sarai bata fad'in abinda tasan bazata aykataba, bashida zab'in daya wuce yabi umarninta,shiryawa yayi driver d'inshi da excode d'inshi ne suka masa rakiya yatafi Kaduna.wanda hakan ba k/aramin dad/i yayiwa Surbajo ba.


Se sha daya na rana suka isa Kaduna.

Gidan iyayensa yafara zuwa yasanar dasu abinda yakawo shi sunyi murna sosai dajin zancan fatan alkhairi sukayi masa gamida yimasa nasiha akan yayi adalci atsakanin Matanshi godiya yamusu, mommy tafara tsokanarshi dacewa,

"Allah ya soka bata gama iddah ba data gama sede kashiga layin zawarawanta,"dariya yayi sannan yamusu sallama ya nufi gidansu Aisha.

Yana zuwa yasamu labarin abinda yasameta, hankalinshine yatashi dan bayason ganin wani na wahala sabida shi, Asibitin yanufa sanda yaga Aisha jiri ne yad'ebeshi ze fad'i da sauri excode d'inshi suka tareshi.

Kuka Al-ameen yake sosai tausayi da soyayyar Aisha ne suka shiga zuciyarshi akaron farko fad'i yake, "Aisha kiyafeni bansan halin dakike cikiba namaida igiyar auranmu guda biyu dasuka rage don Allah kitashi wlh ina k'aunarki inkika mutu bazan yafewa kainaba please,"ko motsi Aisha batayi batama san yanayiba abinda ya sake karya zuciyarshi kenan yadunga kuka kamar yaron daya rasa uwarsa.

Likitane yamasa bayani gameda cutar Aisha kuma yabashi shawara akan Inde da hali to afitar da Aisha kasar rasha domin duba lafiyarta.,Al-ameen yagamsu da shawarar likitan dan haka tun agurin yakira wayar masu yimasa visa inze fita yace yanason visa zuwa rasha nanda Kwana biyu ko nawane ze biya na mutum biyar yakeso yau komai dare ze kawo hotunan sauran dan ayi musu passport sabida basu dashi .

Aranan akasa Aisha a motar Asibitin zuwa international hospital dake Abuja tare da rakiyar mamanta da Al-ameen da tawagarsa inda k'annan Aishan aka kaisu gidan su Al-ameen,iyayensa sun tausayawa halin da Aisha take addu'ar samun sauk'i suka mata

Karfe goma na dare suka isa Abuja,adaren yakai hotunan Surbajo,Yusuf,Inna,Aisha,sabida shi yana dashi visa kawai za'a masa banda passport,se sha biyu yashigo gida,Surbajo tafirgita da ganinshi nande yakwashe komai yasanar da ita, kwana tayi tana kuka da sassafe tasa Al-ameen yakaita Asibitin ananne tai kuka bana wasaba dakyar aka rarrasheta. Ranar da ita aka kwana a asibitin fafur tak'i komawa gida.

Da sassafe jirginsu yad'aga zuwa rasha,

to Aisha Allah yatashi kafad'a .

Maman Yusuf

No comments:

Post a Comment