Sunday 16 April 2017

SURBAJO

πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
       *SURBAJO*
πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€


Zahra Muhammad Mahmud


Kuyimin afuwa masoyana wlh raina ne yab'aci Shiyasa na kula.Amman Namuku alkawari bazan sake kulasuba  kugafarceniπŸ™πŸ™πŸ˜­


*Dedicated to, faty axland,rufaida umar, sadnaf,seemaluv,ummu yusura,maryam s bello,duka members na pml this page is yours love you all with all my heart😍😍😍😍😍*


*pure moment of life writers*
         *p.m.l*


*page 91-95*


Al-ameen binsu yayi d'aki dukansu kowacce yay mata fad'a,yaja musu kunne sosai yanuna musu b'acin ranshi,hak'uri sukai ta bashi dakyar ya hak'ura suka koma zamansu kamar da.


Yau Surbajo ce da girki dan haka tun safe take ayki sabida sunk'i yarda ad'aukomusu me ayki ba yarda beyi dasuba amman  fafur sunk'i yarda, se azahar tasamu tagama kintsa komai,da sauri tashiga wanka tafito ta shirya acikin wasu shegun kaya tayi kyau ba kad'anba,d'akin Al-ameen tanufa sabida yakira ta yace mata yadawo.tana shiga da gudu taje tarungumeshi takaimishi kiss, rungumota shima yayi yana Murmushi yace,


"Haba Baby wannan runguma haka ay Seki karyani,koda yake John cena ce ke bakyawa mutum dukan rashin imani",yafad'i yana dariya duka takaimishi sannan tasa kukan ahagwaba tace,

."Wlh bazan yardaba nice John cenar?,kai shikenan kafi son mukyale su suzo su wargaza mana gida, muna zaman lfy su kunno mana bala'i wlh k'aryarsu dole mud'au mataki",tafad'i tana murgud'a masa baki .


Dariya abun yabasa Dan haka rungumota yayi suka fad'a gado yana fad'in,


"Da kyau tawan Shiyasa nake sonki bakya d'aukar non sense, dan haka nima bari nad'au mataki anan, "romance d'inta ya shigayi kota ina tun tana tureshi harde Itama tabi yarima akasha kid'a.

Seda komai yalafa sannan suka sake wani wankan suka shirya suka fito zuwa dinning inda Aisha Itama fitowarta kenan, d'auke da Hanif  d'ayan hannun rik'e da hannun Yusuf,cin abinci sukayi cike daso da k'aunar junansu.



Rayuwa taci gaba da tafiya cigaba ta ko ina zuwa yake musu komai tare yake musu ba banbanci, amman matsayin Surbajo aranshi dabanne yana mata son
 dashi kanshi besan
 iyakarsa ba, kuma Itama haka ko kad'an bata had'a soyayyarshi data kowa, iyayenta yana ganin darajarsu haka Itama tana ganin darajar nasa iyayen, rushe gidansu yayi a rugar  yamusu gini na zamani dede da rayuwarsu,sannan yabasu jari me kyau dansu dunga sana'a, Surbajo har rasa bakin godiya tayi,sede fatan gamawa da duniya lfy data dunga yimasa.


B'angaren Aisha ma rushe gidansu yasa akayi akayi musu gini nagani nafad'a yaba mamanta jari me yawa dan ta dunga juyawa Tana kulawa da yaranta, Wanda hakan yasa Aisha K'ara nadamar abinda ta aykata masa abaya sosai tayi masa godiya har tana kuka.


Surbajo tasake samun wani cikin,Allah sarki Aisha murna takeyi fiye da ma Surbajon, tattali da kulawa daga Aisha har Al-ameen babu irin Wanda basayiwa Surbajo,tun cikin nak'arami Aisha tafara siyan kayan Babies tana tarawa unisex, Surbajo har dariya take mata.


Cikin na wata takwas sukaje scanning akace musu Baby girl ce,Wayyo dad'i rasa inda zasu sa kansu sukayi dan murna.


Siyayya suka shigayi kamar hauka don murnar Baby girl dazasu samu, basu da hira Seta cikin ahaka har Allah yasauketa lfy, tahaifo ta mace me kama da ita sak,babu inda ta barota har gwalo suka dunga yiwa Al-ameen na rashin d'aukoshin da Babyn tayi.

Ranar suna baby taci sunan maman Surbajo, wannan Karon harda Ard'o seda yazo suna jin ansama Babyn sunan masoyiyarsa,suna kiranta da Hanifa.

So da k'aunar da Al-ameen ke nunawa iyalanshi abin koyine ga duk magidanci kud'i basusa yarasa lokacinsuba duk kulawarsa nakansu bashida Lokacin komai senasu da iyayensa.

Lokacin aykin hajji yazo dukansu yabiya musu ta international suka tafi harda yaransu, sunyi addu'oi sosai Akan Allah yaba Aisha haihuwa domin Alfarmar Annabi da Alqur'ani.


Haka ranar tsayuwar arfa ma suka tsaya gurin yin addu'ar,suna kuka Surbajo tafi kowa yiwa Allah kukan yaba Aisha haihuwa domin girmansa.

Lokacin dasukaje d'awafin bankwana da kyar Al-ameen ya b'anb'are Surbajo ajikin Ka'aba tana kuka tana sake rok'on Allah, ahaka har suka dawo gida Nigeria kullum addu'arsu kenan.

Maman Yusuf
πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
         *SURBAJO*
πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€


Zahra Muhammad mahmud



*This page is dedicated to Zahra Muhammad Hausa novels group's nagode da irin soyayyar dakuke nunamin wlh acikin masoyana kune first Allah yasa yadda kuke sona Allah yasa inna mutu ku nunamin irin wannan soyayyar gurin yimin addua ngd banda kamarku yan uwana  sonku ajinina yake love you all from the bottom of my inner heart.😍😍😍😍😍😍😍*


Na jinjina muku..


Mrs fawwaz
Anty khady
 garkuwa
fareeda
feedyluv
Maman sultan
Zee yabour
hafsey
Momyn janan
Maman ihsan
      Kunada yawa wainda kuka dace a jinjinamuku Wanda bankira sunanshiba afuwan abinne da yawa mutuwa tashiga kasuwa,Allah yak'aramuku basira,yakuma d'aukaka pml up up up.   p.m.l backward never insha Allahu.


*pure moment of life writers*
           *p.m.l*


*last page*


*page 96-100*


Allahu gafurur raheem watansu biyu da dawowa Allah yaba Aisha ciki zokuga Surbajo har azumi tayi na nuna godiyarta ga Allah daya amshi addua'rsu,Al-ameen yayi murna sosai itako Aisha harda kukanta gurin nuna godiyarta ga Allah.

kulawar da Surbajo take bata abin gwanin Sha'awa dole su burgeka duk abinda Aisha takeson ci shizata bata ko menene, dayake cikin Aishan me kwad'ayine abubuwa da dama se anbar kaduna za'a samo mata shi in kwad'ayin abunda ba lokacinshi bane a kadunar ya motsa mata.ko kad'an basa gajiyawa da hidimarta wanda ita godiya kawai take musu da fatan alkhairi.

Cikin Aisha se girma yake wanda girman cikin har tsoro yake ba su Surbajo sabida girmane na sose,gashi lafiyarta k'alau ba
ciwon komai se na kwad'ayi gashi yanzu tazama rumbu cin abinci kamar hauka intaci kuma takasa tashi  sesun d'agata.

Watan cikin bakwai suka kwasheta zuwa scanning dan su girman cikin ya tsoratasu,koda sukaje cemusu akayi komai normal kawai de twins ne a cikin.

Wayyo dad'i πŸ’ƒπŸ’ƒSurbajo sujjada take yi tana k'arawa ga ubangiji shiko Al-ameen duk girman Aisha da cikinta be hanashi d'agata ba yana murna.

Daga gurin scanning kasuwa suka wuce suka barta a mota suka shiga wani boutique na babycare suka shiga jidar kaya kamar hauka,daganan gida suka nufa.
Har walima seda sukayi dan murna inda akai addu'ar Allah ya sauketa lfy.

Watan haihuwarta yatsaya kullum cikin addu'a suke Allah ya raba Lfy, wata jumma'a Aisha ta tashi da ciwon nak'uda da sauri suka d'auketa zuwa asibiti.

Da isarsu labour room akasata, Surbajo kamar zatayi hauka dan tausayin Aisha, addu'a kawai sukeyi dan shima oga hankalinshi atashe yake.

Suna nan tsaye wata nurse tafito tamusu albishir data haihu Lfy ansamu twins duka mata,rungume juna sukayi Surbajo da Al-ameen suna nuna farincikinsu ga Allah.

Bajimawa aka fito da me jego da twins d'inta kyawawa dasu aka kaisu d'akin hutu.Surbajo tunda ta d'auki yaran kasa ajiyesu tayi sabida kyan da Allah yay musu kuma abin mamakin yaran da Surbajo suke kama kowa seda yayi mamakin hakan.

Aisha kallon Surbajo tayi murya araunane tace,

"Sister nagode da addu'ar ki gareni,wlh base kin ce kina k'aunataba inda banyarda ke me sona bace yanzu dole nayarda duba da kammanin da yarannan sukeyi dake, nayi imani inba nagartacciyar soyayya hakan bazata yiwuba,nagode miki sister da addu'ar ki gareni Allah ya rabaki da bak'incikin duniya da Lahira,"tafashe da kuka da sauri Surbajo tamik'awa Al-ameen yaran tarungume Aisha tace,

"Haba Aunty yau ranar murnace agaremu ba kukaba Allah ya amshi addu'ar damuka dad'e munayi danhaka godiya kawai zamuyi masa, kimance da komai Aunty na ni mesonkice."

Koda aka Sallamosu Surbajo ce d'auke da yaran tun kan su k'araso gida gidan yacika da y'an uwa kowa murnar haihuwar su twins yake.

Al-ameen yanajin son yaran har zuciyarshi badan komaiba sedan Kama da Surbajo dasukeyi bame kallonsu yace ba ita ta haifesuba, Allah Kenan.

Ranar Suna Surbajo ba k'aramin mamaki tayiba,
   dataji yaran duka sunanta Aisha tace asa musu d'aya Zahra d'aya fatima suna kiransu da mamah da mimah, amman Al-ameen me suna zahran Surbajo yake ce mata yayinda ita kuma yaci gaba da kiranta Babynsa.Surbajo godiya tadunga yiwa Al-ameen da Aisha abisa karar dasuka yimata.


Rayuwa taci gaba da tafiya inda Ahalin yanzu Surbajo tagama university d'inta Amman Al-ameen yace bazatayi aykiba,bata musaba ta hak'ura,Aisha nakan nata karatun dan itama tuni takoma makaranta,Yaransu gwanin Sha'awa bame gane wannance Mamana acikinsu sabida duk kulawa d'aya suke basu.

Al-ameen hankalinshi akwance na iyalanshi ma haka so da k'aunar dake tsakaninshi da Surbajo se son barka duk da yana b'oyewa gudun kar ran Aisha ya b'aci,amman son da yakewa Surbajo gagara misaline.


ina labarin su Ruky?

Ruky tunda suka bar gidan Aisha da wata uku tafara jin canje canje ajikinta dan haka ta nufi asibiti gwajin farko aka bata sakamakon HIV,yanke jiki tayi tafad'i sumammiya Gado aka bata a asibitin.Zuly nasamun labari tazo asibitin tagaida Ruky kamar abin arzik'i daga k'arshe se cewa tayi.

" Wannan k'awance  namu ina sonshi tunda gashi nayi nasarar saka miki ciwon danake d'auke dashi."daganan takwashe labarin komai tafad'a musu tana dariya, Maman Ruky shak'e Zuly tayi kamar zata kasheta tana yimata Allah ya isa,likitoci sunkasa kwaceta a hannunta dan haka suka kira police sukayi gaba da Zulyn.

Ruky ko kuka take me tsanani tashiga barin wasiyya tace ma mamarta tanemarmata yafiyar Aisha tasan hakkintane yake bibiyarsu don Allah tayafemata,ranar Ruky bata sake kwanan duniyaba tace ga garinku bayan tayi kalmar shahada.Allahu akbar Allah nason masu tuba Allah kasadamu da rahamarka dan darajar Annabi da alqur'ani Ameen.

Zuly ko kotu aka shigar da ita k'ara inda aka yanke mata d'aurin rai da rai agidan kaso,gamida horo me tsanani har iya k'arshen rayuwarta. Duniya kenan shiyasa akace abinda kashuka shi zaka girba Allah yasa mudace Ameen.


Su Aisha dasuka sami labarin mutuwar Ruky har gida sukaje gaisuwa ananne mamar Ruky take sanar da Aishan sak'on Rukyn,kuka Aisha tasa tace,

"Wlh nayafe mata duniya da lahira Allah yajik'anta yakyauta namu zuwan,"
godiya yan uwan Ruky sukai tayiwa Aishan.

To Ruky Allah yajik'anki yasa kin huta ya yafemiki kurakuranki.

Surbajo uwar biyu yanzu haka wani cikinne ajikin Surbajo tsoho yafi na Aisha girma scanning na farko aka shaida musu yan biyu ne duka mace da namiji,fad'in murna da farincikin da Al-ameen da Aisha sukayi page din yayi kad'an se fatan Allah ya sauketa Lfy.

Tahaihu  Lfy inda yaran suka ci sunan iyayen Al-ameen. So da k'auna agurin Al-ameen da Surbajo abin fatane ga kowacce mace agidan mijinta.


*Godiya ga Allah subuhanahu wata'ala daya bani ikon kammala wannan littafi nawa me suna Surbajo.ya Allah kuskuran danayi kagafartamin wa'azin dake ciki gamu mata masu zafafa k'iyayyar kishiya Allah yasa mata sund'auki darasin, maza mata masoyana ako ina kuke afad'in duniya me surbajo na k'aunarku harcikin ranta Allah yabarmu damasu son mu ameen wandama baya sonmu Allah ka jarabceshi da sonmu,Allah yazaunar damu cikin aminci. Kubiyoni cikin sabon littafina mesuna CIN AMANA KO FANSA*

NGD


maman Yusuf love you all πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹

No comments:

Post a Comment