Sunday 26 March 2017

SURBAJO

[3/26, 06:58] Zahra muhd mahmud💃: 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
         *SURBAJO*
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀

Zahra Muhammad mahmud


*page 43-44*



Tana idar da sallar su Usman suka shigo gaisheta sukayi hadi da Mata yajiki
Amsawa tayi cike dajin kunya

Dubata Hafsat tasakeyi daganan tahado magani taba alameen tamasa bayanin dosage din

Kara Jan kunnenshi tayi sosai akan yakyale surbajo ta huta godiya yamata daganan tace zasu iya tafiya gida kuma surbajo tayawaita zama cikin ruwan dumi da gishiri


Kamo mata hannu yayi yamikar da ita suka fara takowa a hankali surbajo se rintse ido takeyi sabida zafin datakeji

Suna zuwa mota gidan gaba yabude mata sannan yayi adjusting din sit din dantaji dadin zama

Hafsat da Usman har gurin motar suka yomusu rakiya sunata tsokanarshi
Kala becemusuba illa tada motarshi dayayi yafice daga gidan


Yana driving hankalinshi nakanta koya tamotsa zece sannu babyna am really sorry ahaka harsuka karaso gida

Tundaga kan megadi zuwa sauran maaikatan gidan gaisheshi suke suna yame jiki Dan sun fahimci madam dinshi ba Lafiya shiyasa yafita agigice

Alameen koda yafito daukar surbajo yayi Dan yanayin tafiyaRta kadai yaisa yatona asirin abinda yafaru shiyasa yadauketa gudun faruwar hakan a idon yaranshi


Adakinta yaajiyeta sannan shima yazauna bayan yajawota jikinshi land line din dakin yadaga yakira kitchen cikin harshen turanci yabasu oda game da kalar abinci dazasu girka musu

yana katse wayar yakai dubansa gun surbajo wacce Tunda yasoma wayar takafeshi da ido huremata ido yayi yana dariya yace yadai baby wannan kallonfa
Rufe ido tayi Tana murmushi  tace kado Yaren dakakeyine yayimin dadi nima ka koyamun

Murmushi yayi gamida shafo fuskarta yace maze hana inde turancine sekin gaji dashi
Godiya tamasa sosai cike da farinciki


rayuwa taci gaba da tafiya alameen iya karfinsa yake kulawa da surbajo harta warke sosai kotayi barna bayama nuna yagani sede cikin dabara zekoyar da ita abinda bata iyanba kuma cikin hukuncin ubangiji duk abinda yakoyamata bata mantawa taRikeshi kenan
Yasha kiran waya yabata su gaisa dasu mommy da daddy itako Aisha koya kirata bazata dagaba Dan fushi take dashi bana wasaba


Yauma kamar kullum suna zaune afalonshi surbajo tayi matashin Kai da cinyarshi suna kallo gefe daya kuma plate din naman kazane alameen keci Tunda aka kawo yake nacin surbajo tatashi taci naman Amman taki wai ita bataci
Yanacikin ci kamshin kazar yagama buwayar surbajo Dan daurewa kawai takeyi dagudu tamike tashiga toilet tafara kwara amai jin karar Amaine yasa alameen rugawa bayin riketa yayi harta gama aman yawankemata baki yafito da ita kan gadonshi yakaita yakwantar sannan yaje yagyara inda tabata

Gurinta yadawo yaga Tana rawar sanyi dasauri yaja bargo yarufeta can kasakasa tace kado Don Allah kafitar da namancan aradu banason kamshinshi
zuciyata tashi takeyi

mamaki ne yakamashi dajin zancanta duba da ganin ita din meson namace Amman yau itake korar nama daga kusa da ita lalle abunda mamaki

daukar naman yayi yafita dashi sannan yadawo koda yataba jikinta zazzabine me zafi ajikinta

hankalin alameen ne yatashi dasauri yadaga waya yakira Usman dayake weekend ne yasan maybe yana gida
ko gaisuwar Usman beamsaba yace frnd Don Allah katuro mana Hafsat surbajo batada Lafiya sosai Wlh
mekamata Usman yatambaya
haba frnd meko zanmata Wlh rashin Lafiya ne kawai

OK to shikenan gamunan zuwa

baadadeba segasu sunzo shida Hafsat dauke da kayan aykinta nandanan Tashiga gwajegwaje inda batasha wahalaba tagano ciki Dan wata biyu makale a marar surbajo abin yabata mamaki matuka

bayani tayiwa alameen tahanyar cewa albishirinku Dan dukanku sekun bani goro to kanwata surbajode cikine da ita harna tsawon sati takwas.

kallon kallo suka tsaya sunayi tsakanin shida Usman
hawayene suka fara bin fuskar alameen na farinciki da fargaba magana yafara dacewa hakika Hafsat kindace daabaki goron albishir Amman fargabata shine nikaina kince nadena kusantarta to taya kuma da zefito daga jikinta dariya Hafsat tayi sannan tace wannan kuma ikon Wanda yasa cikin ajikinta ne wannan badamuwabane zuwa lokacin dazata haihu ayta Kara girma Dan haka kakwantar da hankalinka wannan mesaukine
Usman yakaraso kusa da alameen yana dariya yadafashi yace Kai friend wannan kaine sharp shooter din bugu daya se kwallo araga gaskiya natayaka murna you are going to be a father gaskiya nayi murna

sundade agidan sannan suka musu sallama bayan Hafsat tarubuta Maganin dazaa siyowa surbajo

rakosu yayi sannan yaba driver dinshi kudi da takardar Maganin yace yaje yasiyo masa yanxunnan

gida yadawo gurin surbajo wacce batasan wainar daake toyawaba sabida bacci takeyi
karasawa yayi inda take yazauna agefenta fuskarshi dauke da murmushi rigarta yadaga yadora hannunshi amararta ransa namasa sanyi Ashe shima yanada rabon ganin jininsa aduniya wasu hawayenne nafarinciki suke biyo fuskarsa. toilet yashiga yadauro alwala yazo yayi nafila Tanuna godiyarsa GA Allah dawannan kyauta dayamasa
yana idarwa aka kawo Maganin Ta yatasheta yabata kamin dare harta warware alameen se tattalinta yakeyi Amman befadamata abinda ke damuntaba itama bata tambayaba Tunda taji taji sauki

Maman Yusuf
[3/26, 09:59] Zahra muhd mahmud💃: 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
         *SURBAJO*
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀


Zahra Muhammad mahmud


*page 45-46*


Cikin surbajo me laulayine sosai gabadaya yasata agaba ko ruwa tasha seyadawo komai bata iya ci se in alameen yatakuramata sannan takeci tanagamawa kuma zata amayar dashi
Sosai alameen yake tausayamata Dan sotari yasha yimata kuka intana amai

GA surbajo badauriyar ciwo koya yake tadunga kuka kenan

Ko office yaje bashida natsuwa sabida yasan surbajo dakin shan Maganin inde bashine yabataba bazata shaba shiyasa ko yana office yake zuwa yabata yakoma.

Cikin yakai wata hudu yanzu alhamdulillahi babu ciwon dake damunta sedan banzan kwadayi harda na banza kome nene inde dangin gishiri da magine tofa bazata barshiba setaci gaci kamar gara yanzu zataci  abinci yanxu zata sake jin yunwa alameen shikanshi yanzu yasamu sauki inde yahadata da duk abinda take so bashida Matsala har yaje yadawo


Yau da wuri alameen yadawo gida tundaga falo yake jiyo sautin kukan surbajo dagudu yakarasa dakinta

akwance yatarar da ita Tana kuka harda bubbuga kafa Tana kuka dasauri yakarasa yadagota  yana tambayarta Lafiya cikin kuka tace kado aradu kadangare ne acikina se motsi yakemin narasa yadda zanyi yaki denawa  rungumota yayi yana shafa bayanta yace ayya sorry baby ba kadangare bane kinji baiwa ce Allah yamiki sabida kar mutuwa tazo gurinki shine Allah yabaki wannan yazama kariya agareki dasauri surbajo takalleshi Tana share hawayenta tace kado to se yaushe zandenajin motsin
Kara rungumota yayi yana shafa cikinta Wanda yadan fara tasowa yace baby ay baiwar da Allah yamiki itace abinda ke cikinki da ne Wanda zaki haifamana yar baby kidunga yimata kitso da kunshi kimata wanka da kwalliya ko bakyaso
Dasauri surbajo ta Mike tsaye tace kado da gaske Kake zan haifi yarinya kai yagyada mata ay surbajo bata jira komaiba tafara rawa Tana rera Waka iya karfinta ita ala dole zata zama uwa

rukota yayi yace baby to ay inkina tsalletsalle cikin fadowa zeyi dasauri tasa hannu ta tare cikin gudun kar yafadi abun dariya yaba alameen yace to kinemi guri kizauna
Fir surbajo taki daga kafarta dasunan tafiya wai ita intayi tafiya cikinta zefadone Dan haka aradun Allah bazata takaba
dole alameen yadauketa yazaunar koda tazauna bata saki cikinnataba

Tundaga ranar ayki yadawowa alameen sabo Dan surbajo fafur taki yarda tayi tafiya da kafarta gudun kar cikinta yafadi tattalinshi take bana wasaba inyana motsi dadi takeji itama zata Haifi ya

koda lokacin awon ta yazo har gida Hafsat take zuwa tayimata ko alameen yakaita ayimata tabara iri iri yinta suke dagashi har surbajon dansesu share fin awa guda suna hira da dannasu naciki

siyayyar haihuwa kuwa tuni alameen yafara komai yagani na yara seya siya inyakawo surbajo taita murna. sosai suke kaunar cikin babu kamar alameen   Dan yafi surbajo dokin cikin

yau dawata matsananciyar Shaawa alameen yatashi yarasa yadda zeyi daurewa kawai yakeyi Dan beson yakara kusantar surbajo Dan tausayinta yakeji kuma dama Tunda yayi nafarkonnan besakeyi ba

mararshi harta soma rikewa suna zaune da itane dama yana matsamata kafafuwa mikewa yayi yacemata  yana zuwa

dakinshi yashige yaje yakwanta mararshi naciwo sosai addua kawai yakeyi yarasa ina zesa kansa


surbajo jin shurun tayi yawa bedawobane yasata fara rarrafawa zuwa cikin dakinnashi can tasameshi kwance akasa yanata nishi dasauri takarasa gurinshi taruko hannunshi arude tace kado meyasameka dakyar Yace baby mutuwa zanyi

wayyo nashiga uku kado karmuyi haka dakai aradu kamutu ruga zasu maidani surbajo tafadi Tana kuka tarungumoshi tace  kado kaga kuma inasonka ga kuma yaronmu ko yarinya kace kaine babanshi inka mutu dawa kakeson muzauna Dan Allah kafadamin Maganin dazan baka karka mutu

rukota yayi dakyar yace baby Maganin najikinki kece kawai zaki bani nawarke kin amince nadauki Maganin Kai tadaga masa dasauri aranta cewa take Tunda itama yataimaketa yabata sirrin dauwama aduniya aradu komenene shi zata bashi Shima kar yamutu

rukota yayi yafara kissing dinta takoina tuni surbajo itama tashiga maidarmishi

ahankali yadunga binta har yasamu yabiya bukatarshi jiyayi duk wata cuta tarabu dashi dagowa yayi yana kallon surbajo wacce se murmushi takeyi ita kadai Dan gaskiya taji dadin abunda yamata matsowa kusadashi tayi tace kado aradu Maganin mutuwarka me dadine nibanso ka warke da wuriba

dariya ce takwacewa alameen can dabara tafadomasa yace to aykece baki Saniba shi wannan abun shize dunga sawa babynmu yadunga girma kuma kema zekara tsaremiki ranki

washe baki surbajo tayi tace iko se Allah yanzu kullum zamu dunga yikenan
eh mana inkinaso alameen yabata amsa dasauri tace aradu inaso

tundaga wannan rana alameen da surbajo suka dinke sosai yake samun biyan bukatarsa agurinta badare ba rana kafi shayi ma baya wuceshi yanzu har wata kiba yafarayi sabida hankalinshi akwance yake ga surbajo yanzu kauyancinta dasauki Dan har waya yasiyamata kuma yana koya mata yadda zatayi amfani daita burinshi Allah yasauketa Lfy Yasata a school dan yanzu wata malama yadauko take mata lesson agida kuma ba laifi Tana kokari Dan har mamaki abun yake bashi Dan surbajo akwai kokari


cikin surbajo nawata bakwai alameen yasamu pass natafiya gida Danhaka shiri suke natafiya gida kasuwa yashiga yakarasa siyo kayan baby sabida surbajo tayi scanning  inda akace musu tamace Zata haifa murna gurinsu baa magana

ranar jummaa suka dau hanyar kaduna suna sauka a airport  excode dinshi najiransu kai tsaye gida suka wuce koda suka isa gida Aisha batanan Dan haka wanka sukayi suka ci abinci suka zauna afalo suna hirar

se azahar Aisha tashigo gidan arba tayi da surbajo da katon ciki agaba alameen namatsamata kafa su basu lura da itaba se jin karar faduwar Abu sukayi dasauri alameen yanufo gurin Aisha yagani asume dasauri yadauko ruwa ya yayyafamata seda tajima sannan tafarko kuka takeyi bana wasaba kwace jikinta tayi tashige dakinta Tana kukan takira Ruky tafadamata abinda tagani cemata tayi inzata iya fitowa yanzu tazo su hadu agidan su zuly.


maman yusuf
[3/26, 11:01] Zahra muhd mahmud💃: 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
        *SURBAJO*
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀


Zahra Muhammad mahmud



*page 47-48*



Mikewa tayi tadauki gyalenta da Jakarta tafice suna zaune afalo tazo tawucesu ko kallo basu ishetaba

Alameen mikewa yayi yadauki surbajo suka shige daki wanka yamata shima yayi suka shirya yadauki tsarabar iyayensa da yanuwansa yajata suka fita zuwa gidansu

Suna shiga gidan Da munawwara suka fara cinkaro ay Tana ganin surbajo da katon ciki dariya tafarayi sannan taruga da gudu dakin mummy tamata albishir

Duka mutanen gidan sun hallara afalo se tattalin surbajo sukeyi musamman mommy wacce tausayimnta takeji shima daddy baa barshi abayaba kowa sonta yakeyi kabeer ma da matarsa da yaransa zuwa gidan sukayi anata yiwa juna barka tare da adduar Allah yasauki surbajo Lafiya


Aisha Tana zuwa gidan su  zuly taje Tana zuwa ta tarar suna jiranta ko zama batayiba suka dunguma zuwa gurin wani hatsabibin boka
Tunkafin su fadamasa abinda yakawosu shi yashaida musu wata muguwar dariya Yayi yace wannan mesaukine yanzu mekukeso ayimuku
Dasauri Aisha tace sonake akashe abinda ke cikinta ni inda halima ahada harda ita

dariyar mugunta yayi sannan yace baze yiwu akashe uwarba Amman abin cikinta sede wani Amman bawannanba

waTa laya yabasu yace su wurga ta acikin tsohuwar rijiya ladan aykinshi kuma baa biya se bukata ta tabiya godiya suka masa suka Baro gurinshi
Basuje gidaba seda suka sami rijiyar suka wurga layar sannan kowa tanufi gida


da daddare surbajo nakwance ita kadai dayake alameen dakinshi yakwana gudun karyayi rashin adalci

Tana cikin bacci tayi mafarki ga bera nan akusa da ita farkawa tayi agigice koda tafarka se ganin wata katuwar bakar mage tayi akusa da cikinta akwance salati tayi dagudu magen tashige kasan gadonta surbajo sakkowa tayi daga kan gadon takulle kofar dakin takoma Dayan dakinnata ta kwanta

Koda safiya tayi alameen yazo dubata labarin abinda yafaru
Jiya tabashi dakinnata yanufa yabude yaduba koina babu magen babu alamarta dawowa yayi yacema surbajo shibega komaiba itako dagewa tayi Tana dakin Dan ta kulle kofar magen naciki Dade yaga bata kwantar da hankalintabane shine yafita yadawo yace yakori magen



Cikin surbajo har yafita awatannin haihuwarsa Amman shuru kakeji ko alamar nakuda babu atattare da ita sannan kuma abinda ke cikinnata baya motsi Dan haka suka nufi asibiti scanning akamata inda aka tabbatarwa alameen abinda ke cikin matarsa yamutu sede hakuri

Hankalinsa inyayi dubu yatashi tunaninsa taya zaa raba surbajo da gawar abinda ke cikinta. Itako surbajo batasan dawar garinba Dan da turanci aka fadawa aminun abinda ke faruwa

Daukota yayi sukaje gidan iyayensa bayani yamusu da turanci gudun kar surbajon taji
Hankalinsu yayi matukar tashi danba mommy ba hatta daddy seda yazubda kwalla

asibitin suka koma dukansu aka kwantar da surbajo awani daki na musamman sannan akasa mata kwayar dake bude bakin mahaifa

wayyo Allah na lokacin da kwayar tasoma aykinta duk wani me imani yaga halin da surbajo take seya tausayamata tun Tana kuka har kukan yadena fitowa alameen ko seda aka rirrikeshi kuka yake tamkar yaro karami

surbajo rai ahannun Allah kowa yaganta seya koka tawahala iya wahala likitocin sunyi iya yinsu amma haihuwa shuru

wani malamin almajirai daddy yakira yamasa bayanin halin da surukarsa take ciki kwantarwa da daddy hankali yayi sannan yace gashinan zuwa

baajimaba malamin yazo aka shiga dashi inda surbajon take Addua yayimata akanta sannan yabada wani ruwan rubutu yace abata Tasha sannan yafito daga dakin yarage daga ita se nurse  da mommy rubutun mommy tabata dakyar Tasha aykamar jira ake tasha ciwon yatashi gadan gadan
da mararta tawani murda ihu tasa gamida kiran sunan kado❗❗❗❗❗❗❗

dagudu alameen yafada dakin shigarshi tayi dede da fitowar kan yar

karasawa yayi yarike mata hannu Yana tofa mata addua
nurse zuwa tayi daniyar karasa jawo yarinyar Amman ina ay yarinyar tarube aciki intajawo sekan yayi kamar ze tsinke dole tabari

wata nurse dince tazo tadunga danno cikin daga saman hakarkarinta itakuma dayar Tana ja dayarda Allah dakarfin ikonsane yafito da yarinyar daga cikin surbajo gaba daya tayi baki sabida ta fara rubewa aciki
karasa ciro mahaifar sukayi wacce irama baki tayi
surbajo se kirari takewa Allah tace lalle Allah yayi gaskiya inda yace ze fitar da rayayye acikin matacce kuma yafidda matacce acikin rayayye
gyarata akayi kamar bata haihuba alameen ko kobinsu daddy zuwa birne babyn beyiba yana makale da surbajo yana kulawa da ita Dan harga Allah tausayintane yakamashi danko daya ce takalli babyn  kasawa tayi se kuka takeyi tanama babyn addua har aka wuce da ita  surbajo kuka kawai takeyi

sedare aka sallamesu tuni ankira dangin mamanta ansanar dasu ruga ma direba aka tasa yaje yafadomusu
gidan iyayensa aka wuce da ita
koda su Aisha suka samu labarin abinda yafaru farinciki kamar zekashesu sosai suka ji dadi danhar party  suka hada na murnar mutuwar yarinyar

surbajo Tana samun kulawa yarda yakamata sumaye tazo daga ruga harda Ardo Amman shi bakwana yayiba duba jikin surbajo yayi yakoma dangin mamantama kullum se sunzo duk abinnan ko leke Aisha batayiba
haka akaita kulawa da surbajo hartayi arbain duk sanda ta tuno babynta setayi kuka alameen shima wani lokacin kukan yakeyi


koda hutunshi yakare zekoma gurin ayki da surbajo yatafi koda suka koma patakot
makaranta yanemamata inda yanemi alfarmar asata a ss1tunda ba laifi lesson din daake mata Tana kokari bamecewa bataje makarantaba
certificate din primary Tana cikin zuwa makarantar taje tazana common interers
dasauran dalibai masu shirin fita daga primary haka shima junior waec
surbajo tamaida hankalinta sosai akan karatunta kuma tanajin dadin karatun duk inda bata ganeba alameen kekoyamata

abangaren zamantakewar aure alaameen besake neman wani Abu agurintaba Dan tausayinta yakeyi sede Dan wasanni dabaa rasaba


maman yusuf

No comments:

Post a Comment